Shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya aike da sakon ta'aziyya, game da hadarin jirgin saman kasar Indonesia ga shugaba Joko Widodo na kasar.
Shugaba Xi wanda ya aike da sakon a Talatar nan, ya bayyana kaduwa, game da rasuwar mutane 189, dake cikin jirgin saman kamfanin Lion na Indonesia.
Cikin sakon na sa, shugaba Xi ya ce hadarin jirgin saman ya tayar da hankalin sa. Ya ce a madadin shi kan sa, da gwamnatin Sin da jama'ar ta, yana mika sakon ta'aziyya ga wadanda hadarin ya rutsa da rayukan su.(Saminu)