in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ma'aikatar kasuwancin Sin ta shirya taron manema labarai game da halartar shugaba Xi Jinping bikin bude taron CIIE
2018-10-29 13:53:38 cri
Yau Litinin, ma'aikatar harkokin kasuwancin kasar Sin ta shirya taron manema labarai na cikin gida da waje, inda wakilin kula da shawarwari kan cinikin kasa da kasa kana mataimakin ministan kasuwancin kasar, Fu Ziying ya gabatar da abubuwan da suka shafi halartar shugaban kasa Xi Jinping bikin kaddamar da taron baje-kolin kayayyakin kasa da kasa da ake shigowa dasu kasar Sin(CIIE) karo na farko.

Fu ya bayyana cewa, shugaba Xi Jinping shi kansa ya bada shawara tare kuma da sanarwa duniya cewa, kasar Sin zata shirya babban taron baje-kolin kayayyakin kasa da kasa da ake shigowa dasu kasar Sin karo na farko daga ranar 5 zuwa 10 ga watan Nuwambar bana a birnin Shanghai. Xi Jinping zai halarci bikin kaddamar da taron gami da halartar sauran wasu muhimman ayyuka, haka kuma, akwai manyan shugabanni da jami'an gwamnati da mutane daga bangarori daban-daban na kasashe da yankuna kimanin 150 wadanda za su halarci taron.(Murtala Zhang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China