Fashewar wani bututun man fetur da sanyin safiyar jiya Juma'a, ta yi sanadin mutuwar mutane a kalla 19 a kauyuka biyu na yankin karamar hukumar Osisioma, na jihar Abia dake kudancin Nijeriya.
Shugaban rundunar tsaro da wanzar da zaman lafiya ta Civil Defense a jihar Benito Eze ne ya tabbatar da adadin wadanda lamarin ya rutsa da su ga kafafen yada labarai a Umuahia, babban birnin jihar.
Benito Eze ya ce, mutane 16 ciki har da mace guda ne hatsarin ya rutsa da su a kauyen Umuaduru, inda wasu matasa a yankin ke dibar man fetur daga bututun da aka lalata.
A cewar shugaban rundunar ta Civil Defense, wasu mutane 3 kuma sun mutu sanadiyyar gobarar da ta tashi a wani gida dake yankin kauyen Umuimo.
Tuni rundunar ta aike da jami'anta don killace wurin don kare karuwar hatsarin. Daga bisani dai jami'an kwana-kwana sun yi nasarar kashe gobarar. (Fa'iza Mustapha)