Yau kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Lu Kang, ya bayyana a yayin taron ganawa da manema labaran da aka saba yi a nan birnin Beijing cewa, wasu kamfanoni da mutane na kasar Amurka, suna yada jita-jitar wai kasar Sin, ta yi satar bayanan sirri ta yanar gizo, inda suka zargi kasar Sin kamar yadda suke so, a don haka gwamnatin kasar Sin ta bukaci gwamnatin Amurka da ta daina yin haka, saboda hakan zai lalata moriyar kasar Sin, haka kuma zai gurgunta huldar dake tsakanin kasashen biyu.(Jamila)