Yau Talata shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gana da takwaransa na kasar Angola Manuel Lourenso a babban dakin taron jama'a dake nan birnin Beijing, inda suka yi shawarwari a tsakaninsu.
Xi ya jaddada cewa, kasarsa ta goyi bayan kokarin da al'ummun kasashen duniya suke yi domin nuna adawa da tsoma bakin da sauran kasashen duniya suke yi wa harkokin gidan kasashensu, tare kuma da samun ci gaba yadda ya kamata. Kana yana fatan hada kai tare da kasashen Afirka domin aiwatar da nasarorin da aka cimma yayin taron kolin Beijing na dandalin tattaunawar hadin gwiwar dake tsakanin Sin da Afirka, ban da haka kuma, yana fatan sassan biyu za su kara karfafa hadin gwiwa dake tsakaninsu a fannonin al'adun gargajiya da masana'antu, ta yadda za su samu moriya tare.
A nasa bangare, shugaba Lourenso ya bayyana cewa, dadadden hadin gwiwar dake tsakanin Sin da Angola ya taimaka ga ci gaban tattalin arzikin kasar, yana fatan sassan biyu za su kara karfafa hadin gwiwa a fannin gina kayayyakin more rayuwar jama'a da inganta rayuwar al'ummar kasar, ta yadda kasar Angola za ta samu ci gaba bisa taimakon kasar Sin.(Jamila)