in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin ta yi watsi da zargin da mataimakin shugaban Amurka ya yi mata kan batun Taiwan
2018-10-05 20:28:57 cri
A jiya ne mataimakin shugaban kasar Amurka Mike Pence ya zargi kasar Sin kan batutuwan Taiwan, Tekun Kudancin kasar Sin, hakkin dan Adama da na addini da sauransu.

Dangane da wannan batu, kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Hua Chunying ta bayyana cewa, kasar Sin daya tak ce a duniya, kuma yankin Taiwan wani bangare ne na kasar Sin, wanda ba za a iya raba shi daga kasar ba. Haka kuma Tekun Kudancin Sin da ma yankin teku dake kusa da su mallakar kasar Sin ce. Kasar Sin tana mai da hankali kwarai kan kiyaye da kuma raya harkokin hakkin dan Adam. Haka kuma, al'ummomin kasar Sin suna da 'yancin bin kowane irin addini bisa dokar kasar. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China