Kasar Sin ta bayyana adawarta ga shirin Amurka na sayarwa Taiwan makamai bisa ko wani irin dalili.
An Fengshan kakakin ofishin dake kula harkokin lardin Taiwan na Majalisar gudanarwar kasar Sin, ya ce kasar ba ta amince da duk wani nau'i na tuntuba tsakanin jami'ai ko sojojin Taiwan da Amurka ba.
Wannan na zuwa ne bayan gwamnatin Amurka ta sanarwa majalisar dokokin kasar matakinta na sayar da makaman da darajarsu ta kai dala miliyan 330 ga Taiwan.
Ya kara da cewa, wadanda suke dagaro kan baki wajen gina kansu da kuma raina zaman lafiya da kwanciyar hankali a Zirin Taiwan, za su gane kurensu. (Fa'iza Mustapha)