in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Manzon musamman na shugaban Sin ya halarci bikin kama aikin shugaban Mali
2018-09-23 16:50:51 cri
Jiya Asabar, shugaban kasar Mali Ibrahim Boubacar Keïta ya gana da manzon musamman na shugaban kasar Sin Xi Jinping, kuma mataimakin shugaban majalisar ba da shawara kan harkokin siyasa ta jama'ar Sin misa Zheng Jianbang, wanda ya halarci bikin kama aikinsa, da na cika shekaru 58 da kasar ta samu 'yancin kai.

A yayin ganawar, mista Zheng ya isar da gaisuwar shugaba Xi ga shugaba Keïta, ya kuma bayyana cewa, tun bayan kasashen biyu suka kulla huldar diplomasiyya a shekaru 58 da suka gabata, kullum suna nuna goyon baya ga juna, kasar Sin na fatan amfani da damar ta tabbatar da sakamakon da aka samu a gun taron kolin dandalin tattaunawar hadin kai a tsakanin Sin da kasashen Afirka da aka shirya a Beijing, don karfafa hadin kai a tsakanin kasashen biyu a fannonin siyasa, tattalin arziki da tsaro da dai sauransu.

A nasa bangaren, shugaba Keïta ya nuna yabo sosai kan shawarar "Ziri daya da hanya daya", da kuma manufar kafa al'umma mai kyakkyawar makoma ga dukkan bil'adama da shugaba Xi Jinping ya gabatar, ya kuma bayyana fatansa na ciyar da dangantakar dake tsakanin kasashen biyu gaba. (Bilkisu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China