in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban Sudan ta Kudu da madugun 'yan tawaye sun tattauna batun zaman lafiya a Khartoum
2018-09-23 16:35:00 cri
Shugaban kasar Sudan ta Kudu Salva Kiir da madugun 'yan adawar kasar Riek Machar a ranar Asabar sun tattauna game da yadda za'a aiwatar da yarjejeniyar zaman lafiyar da aka cimma tun da farko, inji kamfanin dillancin labarai na SUNA.

An jiyo Manawa Peter, kakakin kungiyar fafutukar 'yantar da al'ummar Sudan ta kudu yana cewa, taron ya shafi tattauna batun samar da kyakkyawan yanayi ne a kasar wanda hakan zai bada dama ga shugabannin siyasar kasar wajen shiga a dama da su shirin wanzar da zaman lafiyar kasar.

Ya ce Kiir ya nanata muhimmancin tura mayakan 'yan tawaye na SPLM-IO dasu shiga yarjejejniyar zaman lafiyar.

Kirr ya aikewa Machar goron gayyata, taron wanda zai gudana a Juba, babbam birnin kasar Sudan ta Kudu, kuma ana saran za'a sanya hannu kan yarjejeriyar zaman lafiyar, wanda ake saran mambobin kasashen gabashin Afrika IGAD za su halarta.(Ahmad)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China