in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sudan ta Kudu ta ce takunkumai ba za su yi tarnaki ga burinta na wanzar da zaman lafiya ba
2018-05-31 10:50:54 cri
Sudan ta Kudu, ta ce takunkuman da Amurka ke shirin kakabawa wasu jami'an gwamnatinta, ba za su sauya burinta na cimma wanzar da zaman lafiya a kasar ba.

Kakakin Gwamnatin kasar Micheal Makuei, ya shaidawa kamfanin dillancin labarai na Xinhua jiya a birnin Juba cewa, Gwamnatin ta kuduri niyyar samar da zaman lafiya, duk da barazanar da Amurka ta yi na sanyawa manyan jami'an shugaba Salva Kiir takunkumi.

Jawaban nasa na zuwa ne a lokacin da kwamitin sulhu na MDD za ta kada kuri'ar amincewa da kakabawa wasu manyan jami'an gwamnati takunkumi, ciki har da tsohon kwamandan sojin kasar, a yau Alhamis.

Rikicin kasar Sudan ya shiga shekararsa ta 5. Rikicin dai, ya barke ne a shekarar 2013, bayan sojoji magoya bayan shugaba Salva Kiir da na tsohon mataimakinsa Riek Machar sun gwabza fada da juna. Miliyoyin fararen hula na kasar ne suka tsere kasashe makwabta don neman mafita, yayin da rikicin ke kara kamari duk da yunkurin al'ummomin kasashen waje na kawo karshensa. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China