in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
WHO ta ce har yanzu ana fama da barkewar cutar Ebola a Jamhuriyar Demokradiyyar Congo
2018-09-22 15:59:39 cri
Hukumar lafiya ta duniya WHO, ta ce har yanzu ana fama da barkewar cutar Ebola a Jamhuriyar Demokradiyyar Congo, inda biranen Beni da Butembo suka kasance sabbin wuraren da aka samu barkewar cutar.

Wata sanarwar da WHO din ta fitar, ta ce an samu nasarar takaita yaduwar cutar zuwa sabbin wurare, kuma yanayin na daidatuwa a cibiyar lafiya ta Mabalako dake Mangina na lardin arewacin Kivu, inda kuma a yanzu ayarin jami'an lafiya ke ci gaba da inganta ayyukan takaita cutar a Beni da Butembo, wadanda su ne manyan birane biyu a lardin, domin kare yaduwar cutar zuwa sauran yankuna.

Har ila yau, WHO ta yi gargadin cewa, har yanzu akwai barazanar ci gaba da yaduwar cutar, inda ta ce kalubalen dake akwai su ne na rashin gano wadanda suka yi mu'amala da masu cutar da jinkirin gano cutar a cibiyoyin lafiya da rashin kyawawan matakan kariya da rashin amincewar wasu masu dauke da cutar na zuwa asibitocin da aka ware domin su.

Ta kara da cewa, har yanzu abun da aka mayar da hankali kai shi ne karfafa duk cibiyoyin kiwon lafiya don tunkarar cutar a dukkan yankuna da kuma ci gaba da inganta zama cikin shiri da tunkarar cutar a larduna da kasashe makwabta da babu cutar. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China