Ma'aikatar watsa labarai ta kasar Masar ta sanar da cewa, an kama wani matashi dan shekara 24 mai suna Abdullah Ayman Abdel-Samea a jiya Talata, lokacin da wata kwalba mai dauke da sinadarai dake cikin jakar dake bayansa ta kama da wuta a kusa da ofishin jakadancin Amurka dake birnin Alkahiran Masar.
Sanarwar ta ruwaito kafofin tsaro na cewa, mutumin mai tsattsauran ra'ayi, ya yi niyyar kai hari da kwalbar ce. Lamarin ya faru ne a titin Simon Bolivar kusa da ofishin jakadancin kasar ta Amurka mai cike da matakan tsaro dake tsakiyar birnin Alkahira. Sai dai sanarwar ta ce ba a samu rahoton jikkata ko wata barna ba.(Ibrahim)