in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Habasha na shirin kaddamar da yankunan masana'antu 4 da kamfanonin Sin suka gina
2018-08-29 10:21:23 cri

Nan da karshen shekarar nan ta 2018, kasar Habasha na fatan kaddamar da yankunan raya masana'antu 4 da kamfanonin kasar Sin suka gina a sassan kasar

Kwamishina mai lura da harkokin zuba jari a Habasha Belachew Mekuria ne ya bayyana hakan ga manema labarai a jiya Talata. Mekuria ya ce yankunan raya masana'antun da za a kaddamar su ne: Jimma Industrial Park, da Adama industrial Park, da Dire Dawa Industrial Park da kuma Arerti Industrial Park.

Kaza lika a cewar jami'in, Habasha ta shirya kara yawan jarin da take zubawa, a fannin kere kere, ciki jimillar ma'aunin tattalin arzikin kasar na GDP, daga kaso 5 zuwa kaso 20 cikin dari nan da shekarar 2025, a wani mataki na kasancewa kasa mai karfin masana'antu, wadda ke da matsakaicin kudin shiga a fannin tattalin arzikin ta nan da shekarar ta 2025.(Saminu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China