in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Trump ya soke ziyarar sakataren wajen kasarsa zuwa DPRK saboda rashin samun ci gaban kawar da makaman nukiliya a kasar
2018-08-25 15:47:11 cri

Shugaban Amurka Donald Trump, ya bukaci sakataren harkokin wajen kasar Mike Pompeo, ya soke tafiyar da ya yi niyyar yi zuwa Koriya ta Arewa wato DPRK, yana mai dogaro da rashin samun ci gaba game da batun kawar da makaman nukiliya a zirin Koriya.

Donald Trump ya wallafa a shafinsa na Tweeter a jiya cewa, ya bukaci Mike Pompeo ya soke ziyararsa zuwa Koriya ta Arewa a wannan lokaci ne saboda yana ganin ba su samu gamsasshiyar ci gaba game da batun kawar da makaman nukiliya ba.

Ya kara da cewa, sakatare Pompeo na sa ran zuwa Koriya ta Arewa a nan gaba.

Har ila yau, ya ce ya na mika sakon gaisuwa da ban girma ga shugaba Kim. Kuma yana sa ran ganinsa nan ba da dadewa ba. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China