An damke wani dan Najeriya a filin jirgin saman kasa da kasa na Mohammed V dake Casablanca na kasar Morocco bisa zarginsa da safarar hodar iblis, 'yan sandan Moroccan sun sanar da hakan a jiya Lahadi.
A cewar sanarwar 'yan sandan, an samu hodar iblis din mai nauyin kilogram 1.85 a cikinsa a asibitin Casablanca.
Wanda ake zargin yana shirin tafiya ne zuwa birnin Sao Paulo, na kasar Brazil, in ji majiyar.
A halin yanzu ana tsare da mutumin har zuwa lokacin kammala bincike.(Ahmad Fagam)