in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Jarin da Sin take zubawa a Afirka ya rage gibin karancin kayayyakin more rayuwar jama'a a nahiyar
2018-08-08 13:31:08 cri

Babban darektan cibiyar nazarin manufofin makamashi ta Afirka(ACEP) Benjamin Boakye ya ce, yadda kasar Sin take zuba jari a nahiyar Afirka ya taimaka wajen magance matsalar kayayyakin more rayuwar jama'a na matsakaicin lokaci da nahiyar ke fuskanta.

Haka kuma jarin da take zubawa ya taimaka ga ci gaban nahiyar. Don haka ya shawarci kasashen nahiyar Afirka da su dauki managartan matakai don tabbatar da cewa, an ci gajiyar jarin da kasar ta Sin take zubawa yadda ya kamata, ta yadda nahiyar za ta cimma burinta na samun ci gaba.

Kasar Sin dai tana zuba jari ne a fannonin da suka shafi gina hanyoyin mota, madatsun ruwa, layin dogo wadanda ake ginawa a sassa daban-daban na nahiyar da kudaden da kasar Sin take bayarwa.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China