in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wata kungiya mai zaman kanta ta Sin za ta karrama 'yan Afrika masu kare hallitun dawa
2018-03-20 09:58:03 cri

Kungiyar Paradise Foundation International PFI, dake da mazauni a kasar Sin, ta ce tana shirin karrama 'yan Afrika 50 da suka yi fice wajen kare hallitu da muhallin dawa.

Kungiyar PFI da kungiyar kare namun daji ta gabashin Afrika da kuma asusun Mara Conservation, sun wallafa wata sanarwa a jaridar Star daily, inda suke bukatar a mika musu sunayen wadanda suka cancanci karamawar, wadda ita ce irinta ta farko da kungiyar za ta yi.

Wadanda za su ci gajiyar kyautar dala 3,000 sun hada da masu kare namun daji da dazuka da sauran jami'an dake gaba-gaba wajen kare namun daji da muhallin hallitu da kuma albarkatun kasa.(Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China