Yau Laraba kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Geng Shuang ya bayyana a yayin taron ganawa da manema labaran da aka saba yi a nan birnin Beijing cewa, gwamnatin kasar Amurka tana shirin kara sanya harajin kaso 25 bisa dari kan kayayyakin da za a shigo da su daga kasar Sin, matakan da ta dauka na matsa lamba da yaudara, ba su da amfani ko kadan, idan har ta kara daukan irin wannan matakai, ko shakka babu gwamnatin kasar Sin za ta mayar da martani.(Jamila)