Rahotanni daga Najeriya na cewa, wasu 'yan bindiga sun yi garkuwa da a kalla kauyawa 15, lokacin da suka kai hari cikin karshen mako a yankin Maradun dake jihar Zamfara a arewa maso yammacin kasar.
Kakakin majalisar dokokin jihar Sanusi Rikiji ya shaidawa kamfanin dillancin labarai na Xinhua ta wayar tarho cewa, har yanzu ba a san inda mutanen da aka yi garkuwa da su suke ba.
Ya ce, a baya-bayan nan 'yan bindigar sun kwace a kalla kauyuka da garuruwa a kalla 18 a sama da gundumomin uku dake jihar. A don haka akwai bukatar a sake duba yanayin tsaron da jihar ke ciki.
A jiya Lahadi ne gwamnatin Najeriya ta sanar da tura sama da sojoji 1,000 don magance matsalar hare-haren da jihar ta Zamfara ke fuskanta.(Ibrahim)