in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Xi Jinping ya jaddada cimma nasarar yaki da talauci
2018-07-19 20:44:34 cri
A kwanakin baya ne, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya bada umurni game da harkokin yankin gwaji na Bijie dake lardin Guizhou, inda ya jaddada cewa, sakamakon jagorancin jam'iyyar kwaminis ta kasar, da goyon-bayan bangarori daban-daban, gami da kwazon da jama'a suka nuna, an samu manyan sauye-sauye a yankin Bijie, har ya zama wani abun misali ga yankuna masu fama da talauci don su cimma nasarar yaki da talauci.

Shugaba Xi ya jaddada cewa, ya kamata a zage damtse don tabbatar da ganin an cimma nasarar yaki da talauci cikin lokaci a yankin gwaji na Bijie. Har wa yau, ya zama dole a yi hangen-nesa da bullo da wasu shirye-shirye, don neman samun bunkasuwa ba tare da gurbata muhalli ba, da tsare-tsare da yin kirkire-kirkire a yankin gwaji na Bijie.(Murtala Zhang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China