in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mataimakin firaministan Sin ya jaddada muhimmancin aiwatar da shirin yaki da fatara
2018-06-06 10:41:40 cri

Mataimakin firaministan kasar Sin Hu Chunhua ya bukaci a yi cikakken sanya ido wajen aiwatar da shirin yaki da fatara domin samun nasarar aikin kawar da kangin fatara a kasar.

Hu, wanda shi ne shugaban ofishin kula da shirin yaki da fatara da samun bunkasuwa na majalisar kolin kasar Sin, ya yi wannan kiran ne a lokacin wata ziyarar kwanaki uku da ya kaddamar a lardin Hebei dake arewacin kasar Sin wanda ya kammala ziyarar a jiya Talata.

Hu ya ce, wajibi ne hukumomin kananan yankuna su sanya ido a ko da yaushe kan ayyukan rage radadin talaucin, kana su kara kaimi wajen daukar matakan da za su tabbatar da ganin ana aiwatar da aikin yaki da fatara yadda ya kamata.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China