in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD ta bukaci a taimakwa ayyukan agajin jin kai da farfado da yammacin Afrika da yankin Sahel
2018-07-18 10:13:44 cri
Wakilin Musammam na Sakatare Janar na MDD a yankin yammacin Afrika da Sahel, Mohamed Ibn Chambas, ya bukaci kasashe mambobin majalisar su tallafawa ayyukan agajin jin kai da kuma farfado da yankunan yammacin Afrika da Sahel.

Mohamed Ibn Chambas, ya bayyana haka ne yayin da yake yi wa kwamitin sulhu na majalisar bayani game da ayyukan ofishin MDD a yammacin Afrika da yankin Sahel, da kuma abubuwan dake wakana a yanzu.

Da yake kira ga mambobin majalisar su taimakawa ayyukan jin kai da farfado da yankin, ya ce rikici tsakanin manoma da makiyaya na karuwa kuma babban barazanar tsaro ce da ka iya rikidewa zuwa hare-haren ta'addanci, wadda matsala ce da yankin ke fama da ita a yanzu.

A don haka, ya jadadda cewa, ya kamata duk wani matakin soji na tinkarar kalubalen tsaron ya kasance daidadi da aiwatar da wasu muhimman dabaru dake hada tsaro da agajin jin kai da ci gaba da kuma kare hakkokin bil adama.

Ya kara da cewa, wani batu kuma shi ne, karuwar fashin teku a mashigin Guinea, wanda ya hada da safarar miyagun kwayoyi da na kananan makamai da 'yan ta'adda ke yi, abun da ya bayyana a matsayin babbar barazana. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China