Kamfanin dillancin labarai na SANA ya rawaito cewa, a jiya Lahadi Isra'ila ta kaddamar da harin makamai masu linzami kan sansanin sojojin kasar Syria dake arewacin lardin Aleppo.
Rahotanni sun ce, makamai masu linzamin da Isra'ilan ta harba ya lalata sansanin sojojin sama na arewacin yankin al-Nayrab, kana harin ya yi barna mai yawa.
Harin da Isra'ilan ta kaddamar ya kasance a matsayin martani dangane da irin ci gaban da aka samu na ayyukan soji a kudanci, inda dakarun sojojin Syria suka yi nasarar kwace ikon lardin Daraa na kudancin Syria, ciki har da yankunan dake karkashin ikon 'yan tawaye dake kusa da yankunan da Isra'ilan ta mamaye.
Harin dai shi ne na baya bayan nan daga cikin jerin hare hare ta jiragen sama da kuma makamai masu linzami da aka kaddamar wanda Isra'ilan ta kaddamar kan sansanin sojojin Syria.(Ahmad Fagam)