Kamfanin dillancin labarai na Nijeriya NAN, ya ruwaito cewa, mutum 1 ya mutu, sannan gidaje dari sun lalace sanadiyyar guguwar ruwan sama da aka yi a Dauran jihar Katsina dake arewa maso yammacin kasar, wanda kuma ya kasance mahaifar shugaban kasar Muhammadu Buhari.
Mutane 4 ne suka jikkata inda suke kwance a asibiti, bayan aukuwar lamarin da yammacin ranar Lahadin da ta gabata.
Makamancin al'amarin ya auku a baya-bayan nan, inda ya raba sama da mutane 600 da matsugunansu a yankin, al'amarin da ya sa shugaban kasar Muhammadu Buhari kai ziyarar yini 2 jihar a ranar Juma'ar da ta gabata domin jajantawa wadanda ibtila'in ya shafa.
Wasu jami'ai dake yankin, sun ce ruwan da aka shafe sa'o'i 8 ana yi a garin Daura, ya yi mummunan barna.
A cewar Aminu Waziri, shugaban hukumar kai agajin gaggawa ta jihar, sama da yankuna hudu na garin Daura ne guguwar ruwan ta shafa. (Fa'iza Mustapha)