in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Harin kunar bakin wake ya yi sanadin mutuwar mutane 34 a Nijeriya
2018-06-18 15:41:09 cri

Mutane akalla 34 ne suka mutu, wasu 18 kuma suka jikkata, biyo bayan wasu tagwayen hare-hare da aka kai garin Damboa na jihar Borno dake arewa maso gabashin Nijeriya.

Wani jami'in karamar hukumar da ya nemi a boye sunansa, ya ce bayan tagwayen hare-haren, an kuma kai wani harin gurneti kan mutanen da suka je taimakawa wadanda harin farkon ya rutsa da su.

Yankin karamar hukumar Damboa na da nisan kilomita 88 daga Maiduguri, babban birnin jihar Borno.

Jami'in ya kara da cewa, an kai hare-haren ne yayin da mazauna garin ke komawa gida daga kallon gasar kwallon kafa na cin kofin duniya na bana da aka yi tsakanin Nijeriya da Croatia. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China