in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Guterres ya nuna damuwa game da harin da aka kaddamar kan shugaban Zimbabwe
2018-06-25 09:31:50 cri

Sakatare janar na MDD Antonio Guterres ya nuna damuwa sakamakon harin da aka kaddamar kan taron gangamin jam'iyya mai mulkin kasar Zimbabwe wanda shugaban kasar Emmerson Mnangagwa da sauran jiga-jigan jamiyyar suka halarta.

Hukumomin kasar Zimbabwen sun bayyana harin da aka kaddamar na ranar Asabar a birnin Bulawayo da cewa yunkuri ne na hallaka shugaba Mnangagwa.

Kakakin MDD Stephane Dujarric, ya ce Guterres ya yi Allah wadai da harin, kana ya bukaci a binciko wadanda ke da hannu da kuma gurfanar da su a gaban shari'a, tare da fatan samun sauki cikin hanzari ga wadanda suka jikkata a harin.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China