A kiyaye tsaro da zaman karko
Za a sa himma wajen tabbatar da shirin hadin kai na shekarar 2019 zuwa 2021 na murkushe masu tsattsauran ra'ayin addini, da 'yan aware na al'umma, da 'yan ta'adda na duniya. Nan da shekaru uku masu zuwa, kasar Sin za ta horas da ma'aikatan kiyaye doka da oda dubu biyu ga bangarori daban-daban na kungiyar SCO, a wani kokari na inganta karfin zartas da doka da oda.