in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin ta samar da damammaki na cigaba masu yawa a kasashen Afrika
2018-06-03 15:24:17 cri
Darakatan cibiyar nazarin huldar kasa da kasa da tsare tsare ta Faransa (IRIS) Farfesa Pascal Boniface, ya ce kasar Sin ta samar da damammakin cigaba masu tarin yawa a kasashen Afrika.

Da yake zantawa da kamfanin dillancin labarai na Xinhua a babban birnin kasar Guinea, Conakry, Boniface ya ce, kasar Sin ta samarwa kasashen Afrika damammaki wadanda a lokacin baya basu da su.

Kasar Sin tana cigaba da zama babbar mai ruwa da tsaki ga cigaban Afrika, ya kara da cewa, a da akwai wani nau'in mulkin mallaka wanda kasashen yamma ke yiwa Afrika, kuma shigowar kasashen Sin, Brazil da Japan ya karya wannan tsarin mulkin danniya a Afrikar.

Boniface ya ce, jarin da Sin ta zuba a Afrika ya samar da kyakkyawar makomar cigaba mai yawa, da suka hada da gina kayayyakin more rayuwa, gina filayen wasanni da dai sauransu.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China