in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin tana maraba da dukkan kasashe mambobin MDD da su ci gajiyar tashar binciken sararin samaniyarta
2018-05-29 08:55:39 cri
Jakadan kasar Sin a MDD da sauran kungiyoyin kasa da kasa dake Vienna Shi Zhongjun ya ce kasarsa na maraba da dukkan kasashe mambobin MDD da su hada kai da kasar Sin don cin gajiyar tashar binciken sararin samaniyar da take fatan kafawa a nan gaba.

Jakada Shi ya ce tashar binciken sararin samaniyar( CSS) ba ta kasar Sin kadai ba ce, tasha ce ta duniya baki daya. Don haka dukkan kasashe ba tare da la'kari da girma ko matsayin ci gabansu ba, na iya shiga a hada gwiwa da su ba tare da nuna wani bambanci ba.

Bugu da kari, hukumomin gwamnati da masu zaman kansu dake da sha'awa ciki har da cibiyoyin bincike da masana da jami'o'i da kamfanoni masu zaman kansu masu nasaba da harkokin kimiya, suna iya gabatar da fannonin da za su yi hadin gwiwa da hukumar zartarwas tashar ta CSS,ko ta fannin yadda za a bunkasa tashar ko masaukin 'yan sama jannatin.

Ya ce, a matsayinta na kasa mai tasowa, a shirye kasar Sin ta ke wajen taimakawa sauran kasashe ta yadda za su kara karfin fasahar gina tashar binciken sararin samaniyarsu, musamman fannin binciken sararin samaniya.

A shekarar 2019 ake fatan kaddamar da tashar,kana a fara aiki da ita kadan-kadan a shekarar 2022.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China