in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin ta yi kira da a kai zuciya nesa biyo bayan tashin hankalin Gaza
2018-05-31 14:12:52 cri
Wakilin din-din-din na kasar Sin a MDD Ma Zhaouxu ya yi kira da a kai zuciya nesa bayan da wani sabon fada ya barke tsakanin Palasdinawa da Yahudawan Isra'ila a yankin Gaza.

Ma ya bayyana hakan ne yayin taron da kwamitin sulhun majalaisar ya kira don tattauna sabon fadan da ya barke. Ya ce kasar Sin tana sa-ido kan halin da ake na baya-bayan a yankin, kuma ta damu musamman game da hadarin tsanantar yanayi a yankin na Gaza

Jami'in na kasar Sin ya ce kasarsa na fatan sassan da abin ya shafa za su kwantar da hankulansu, su dakatar daukar duk wani mataki na soja kana su dauki kwararan matakan da za su rage zaman tankiya.

Ko da yaushe kasar Sin na kira da a daidaita rikicin Palasdinawa da Isra'ila ta hanyar tattaunawar lumana, kana bata goyon bayan tashin hankalin da zai kai ga ta'azzara yanayi har ma ya shafi fafaren hula.

Ma ya ce, kamata ya yi kasashen duniya su ci gaba da tsayawa ga manufar warware wannan batu ta hanyar kafa kasashe biyu, kana su yi aiki kamar yadda dokokin kasa da kasa suka tanada. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China