in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ana samun nasara a tattaunawar kasar Sin da Tanzania game da aikin tashar Bagamoyo
2018-05-20 13:19:54 cri
Kasar Sin ta ce ana samun nasara a tattaunawar da ake tsakaninta da Gwamnatin Tanzania game da aikin tashar ruwa ta Bagamayo da yankin tattalin arziki na musammam, da za su lakume dala biliyan 10, al'amarin da zai bada damar fara aiwatar da aikin da aka dade ana jinkirtawa.

Jakadar kasar Sin a Tanzania Wang Ke, ta shaidawa manema labarai a Dar es Salaam, yayin da ta kai ziyara ma'aikatar kudi da tsare-tsare na kasar cewa, ana samun nasara a tattaunawar da ake tsakanin gwamnatocin biyu kan aikin tashar Bagamoyo, inda ta ce aikin na da matukar muhimmanci ga dangantakar dake tsakanin kasashen biyu.

Ta ce Gwamantocin Tanzania da Sin, sun tuntubi juna sosai game da aiki, inda ta ce ta na fatan za su cimma matsaya kan kwangilolin da suka shafi aikin don fara gudanar da shi nan bada dadewa ba, domin al'ummar Tanzania ta amfana.

An rattaba hannu kan matakin farko na yarjejeniyar gina tashar Bagamoyo ne tun a shekarar 2013, sai dai cimma yarjejeniyar karshe game da jarin gudanar da aikin na tafiyar hawainiya. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China