Rundunar 'yan sandan Najeriya ta tabbatar da rasuwar mutane 9, yayin wani harin da aka kaiwa wasu mutane dake hanyar su ta zuwa majami'a a yankin Tutuwa dake karamar hukumar Ussa ta jihar Taraba.
Kakakin rundunar 'yan sandan jihar David Misal, ya ce baya ga wadanda suka rasu, wasu mutane 3 kuma sun samu raukuna, baya ga wasu 2 da har yanzu ba a gan su ba.
'Yan bindigar dai, a cewar sifeton 'yan sandan Ussa Rimansikwe Karma, sun yiwa masu ibadar kwantan bauna ne a kan hanyar su da zuwa coci, suka kuma bude musu wuta, kana suka tsere kafin zuwan jami'an tsaro.
Ko da a ranar 8 ga watan Janairu ma dai wasu mutanen a kalla 12 sun rasa rayukan su, a wani hari na kisan ramuwar gayya da sassan mabiya manyan addinan yankin biyu ke wa junan su a jihar.
Jihar Taraba dai na fama da tashe tashen hankula masu nasaba da neman ikon filaye, da na banbancin addini da kuma kabilanci, lamarin da ya haifar da kisan dubban al'umma a 'yan shekarun baya bayan nan.(Saminu)