in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Guterres ya yi tir da hari a arewa maso yammacin Nijeriya
2018-05-08 09:36:09 cri

Sakatare Janar na MDD Antonio Guterres, ya yi tir da kakkausar murya, kan harin da aka kai wani kauyen jihar Kaduna dake arewa maso yammacin Nijeriya, al'amarin da ya rutsa da mutane da dama.

Sanarwar da kakakinsa Stephane Dujarric ya fitar a jiya, ta ruwaito Antonio Guterres na yin kira da a gaggauta hukunta maharan.

Sakatare Janar din, ya kuma bayyana damuwa game da yadda ake ci gaba da samun tashe-tashen hankula, yana mai bukatar dukkan masu ruwa da tsaki su yi aiki tare, don wanzar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a kasar.

Sanarwar ta kuma ruwaito shi yana jajantawa iyalan wadanda harin ya rutsa da su da kuma gwamnati da al'ummar Najeriya, tare da yi wa wadanda suka jikkata fatan samun lafiya cikin sauri.

A ranar Asabar ne wasu 'yan bindiga suka kai hari kauyen Gwaska na jihar Kadunan Nijeriya. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China