Mutane biyu sun mutu a Abuja, fadar mulkin tarayyar Najeriya bayan bullar cutar zazzabin Lassa wadda ta barke tun a farkon wannan shekara, ta bazu zuwa kusan jihohin kasar 20, hukumomin lafiya na yankin ne suka tabbatar da lamarin a ranar Laraba.
Wani jami'in hukumar lafiya ta yankin Humphrey Okoroukwu, ya ce mutanen da suka mutu na daga cikin wadanda suka kamu da cutar zazzabin a cikin watanni uku a birnin Abuja.
Okoroukwu, wanda ke shugabantar sashen kiwon lafiyar jama'a na Abuja, ya ce an samu rahoton bullar cutar kimanin 38 a birnin, kuma ana ci gaba da gudanar da bincike a kwaryar babban birnin kasar.
A kalla mutane 120 ne aka tabbatar da mutuwarsu sakamakon kamu da cutar kawo yanzu a cikin jihohin kasar 19, ciki har da babban birnin kasar Abuja, tun bayan da aka samu rahoton farko na bullar cutar a ranar 1 ga watan Janairu.(Ahmad Fagam)