in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Rasha ta sanar da korar jami'an diplomsiyyar kasashe 23 dake kasar
2018-03-31 12:49:28 cri
Ma'aikatar harkokin wajen Rasha ta kira wakilan diplomasiyyar kasashe 23 dake kasar, ciki har da na Australia da Jamus da Italiya da sauransu, inda ta sanar musu cewa, kasar za ta kori jami'an diplomasiyyarsu da yawansu ya yi daidai da na jami'anta da suka kora daga kasashensu.

Wata sanarwa da ma'aikatar ta fitar a jiya, ta ce wannan martani ne da Rasha ta mayar ga wadannan kasashen da suka kori jami'an diplomasiyyarta.

Rasha ta bayyana cewa, bisa zarginta da Birtaniya ta yi na sanyawa tsohon jami'inta na leken asirin Sergey Skripal da 'yarsa guba ba tare da tushe ba, kasashen 23 suka tsaida kudurin korar jami'an diplomasiyyarta, a don haka, ita ma za ta kori jami'an diplomasiyyarsu da yawansu ya yi daidai da na jami'anta da suka kora.

Ban da wannan kuma, ma'aikatar harkokin wajen Rashar ta gabatar da sanarwa ta daban a wannan rana, inda ta ce ta kira jakadan Birtaniya dake kasar, don nuna rashin jin dadinta game da matakin Birtaniya na sa kaimi wajen ganin sauran kasashe sun kori jami'an diplomasiyyarta. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China