Da misalin karfe 3 da minti 10 na yammacin shekaranjiya ne gobara ta tashi a rukunin kantuna mai bene hudu na birnin Kemerovo dake jihar Kemerovo na kasar, daga wurin wasan yara dake bene na hudu, inda ta wutar ta ruru zuwa sauran wurare cikin sauri, har ma hayaki mai karfi ya game ko'ina.
Ministan kula da bukatun gaggawa na Rasha ya ce an jajirce wajen gano musabbabin tashin gobarar, yana mai cewa za'a bayyanawa jama'ar kasar da zarar an samu kwararan sakamako,
A wani labarin kuma, sanarwar da gwamnatin yankin na Kemerovo ta fitar, ta ce za a yi zaman makoki na tsawon kwanaki uku a yankin daga yau Talata, domin wadanda gobarar ta rutsa da su. (Murtala Zhang)