in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Putin ya ba da umarnin binciken matakan kariya a rukunonin kantuna bayan gobarar da ta tashi a kasar
2018-03-29 10:39:24 cri

Shugaban Rasha Vladimir Putin, ya bukaci a gudanar da bincike kan matakan kariya a rukunonin kantuna, bayan mummunar gobarar da ta tashi a birnin Kemerovo na yankin Siberia dake kasar.

Sanarwar da fadar Kremlin ta fitar ta ce, Putin ya ba da umarnin ne yayin wani taro kan tattalin arziki da aka yi a jiya.

Da tsakar ranar Lahadi ne wata mummunar gobara ta tashi a rukunin kantuna na Winter Cherry dake birnin Kemerovo na kasar, inda ta yi sanadin mutuwar mutane 64.

Shugaba Putin ya umarci gwamnatin tarayyar kasar da hukumomin yankin, sun ba da dukkan taimakon da ake bukata ga iyalan wadanda suka mutu ko suka jikkata yayin gobarar.

A wani taro na daban da shugaban kwamitin bincike na kasar da ministan lafiya a jiyan, shugaban kasar ya jadadda cewa, tilas ne a gudanar da bincike kan tashin gobarar bisa gaskiya da adalci. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China