in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin na fatan daidaita rikicin tattalin arziki da ciniki tare da Amurka yadda ya kamata
2018-03-15 19:46:45 cri

Yau Alhamis Lu Kang, kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin ya sake nanata matsayin kasar Sin game da rikicin tattalin arziki da ciniki a tsakaninta da kasar Amurka a yayin taron manema labaru da aka saba shiryawa a nan Beijing, inda ya ce, Sin da Amurka sun dade suna tuntubar juna dangane da yadda za a daidaita wannan takaddama. Sin na fatan kasashen 2 za su daidaita rikicin ta hanyar yin hadin gwiwa yadda ya kamata. Lu Kang ya kuma jaddada cewa, abubuwan da suka faru a tarihi sun shaida cewa, yakin ciniki ba abu ne da ya dace da muradun kowane bangare ba. Don haka kasar Sin za ta tsaya kan kiyaye hakkokinta. (Tasallah Yuan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China