in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
WHO ta ce mutane miliyan 3.1 ba su samu damar zuwa asibiti a arewa maso gabashin Najeriya
2018-03-13 09:01:08 cri

Hukumar lafiya ta duniya (WHO) ta sanar da cewa, kimanin mutane miliyan 3.1 a yankin arewa maso gabashin Najeriya ba su samu damar ziyartar asibitoci sakamakon rikicin Boko Haram da ya addabi shiyyar.

Cikin wani rahoton da ta fitar a birnin Maiduguri dake shiyyar arewa maso gabashin kasar, hukumar ta WHO ta ce, an lalata asibitoci da yawansu ya kai 755 a hare haren da mayakan 'yan ta'adda na Boko Haram suka kaddamar a jihohi ukun da hare haren 'yan ta'addan suka fi kamari a shiyyar, da suka hada da jihohin Adamawa, Borno, da Yobe.

MDD ta sanar a watan Yulin shekarar 2017 cewa, kimanin adadin mutane miliyan 6.9 ne ke bukatar tallafin jin kai a shiyyar arewa maso gabashin Najeriyar.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China