in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Majalisar dokokin Afrika ta Kudu ta amince da kudurin karbe filaye ba tare da biyan diyya ba
2018-02-28 09:59:48 cri

Majalisar dokokin kasar Afrika ta Kudu, ta amince a jiya Talata, da tsarin karbe ikon filaye daga hannun wasu mutane ba tare da biyan diyya ba.

Sai dai a cewar kakakin jam'iyyar ANC dake majalisar Nonceba Mhlauli, dole ne a aiwatar da tsarin bisa tabbatar da wadatar abinci da habakar tattalin arziki da kuma sauya tsarin tattalin arzikin kasar tun daga tushe.

Bangaren adawa dai ya nuna kin amincewarsa da batun tilasta sayen fili, yana mai cewa, zai yi nakasu ga ayyukan yi tare da yin barazana ga wadatuwar abinci. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China