Shugaban kasar Afrika ta Kudu Cyril Ramaphosa, ya yi ministocinsa tankade da rairaya jiya da daddare, inda ya sallami wasu daga cikinsu tare da sauyawa wasu ma'aikatu.
Cyril Ramaphosa ya bayyana garambawul din ne yayin wani taron manema labarai da ya gudana jiyan a Pretoria, inda ya ce, yayin aiwatar da sauyin, ya yi la'akari da bukatar dake akwai na daidaita ci gaba da kwanciyar hankali da farfado da tattalin arziki da gaggauta samar da sauye-sauye na ci gaba.
A yau Talata ne ake sa ran rantsar da sabbin ministocin. (Fa'iza Mustapha)