Rundunar 'yan sandan Nijeriya ta fara kokarin kwace makamai daga hannun wadanda suka mallake su ba bisa ka'ida ba da wasu hukumomin tsaro a fadin kasar.
Babban Sufeton 'yan sandan kasar Ibrahim Idris ne ya umarci jami'an rundunar su fara kwato makaman da ake amfani da su ba bisa ka'ida ba.
An dauki matakin ne a kokarin da ake na magance rikice-rikicen dake barkewa tsakanin bangarori daban-daban a wasu sassan kasar, al'amarin dake kai wa ga asarar rayuka da dama. (Fa'iza Mustapha)