Amurka: Tilas ne a kau da makaman nukiliya daga zirin Koriya
Fadar shugabacin Amurka wato White House, ta ce duk wata tattaunawa da za a yi tsakanin Amurka da Koriya ta Arewa, za ta dogara ne kacokan a kan bukatar kawar da makaman nukiliya daga zirin Koriya. Fadar ta bayyana haka ne cikin wata sanarwa da ta fitar jiya Lahadi, inda ta mayar da martani ga niyyar kasar Koriya ta Arewa ta tattaunawa da ita. (Bello Wang)
Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku