Jiya Jumma'a aka kai hare-haren bama-bamai cikin motoci sau biyu a Mogadishu, fadar mulkin kasar Somaliya, daya daga ciki, an kai harin ne a wurin dake kusa da fadar shugaban kasar, an ce, yayin hare-haren, a kalla mutane 18 suka rasa rayukansu, kana saura guda 20 suka ji rauni.
Bisa labarin da hukumar tsaron kasar ta bayar, an ce, a yammacin wannan ranar, da misalin karfe 6, bom ya fashe a cikin wata motar dake kusa da hedkwatar hukumar leken asiri da tsaron kasar ta Somaliya, bayan mintoci kusan 15, an tarwatsa bam da aka ajiye a cikin wata mota kan titin dake kusa da fadar shugaban kasar.(Jamila)