Hua ta bayyana hakan ne a yayin taron manema labaru da aka shirya a wannan rana, inda ta kara da cewa, kasar Sin na adawa da duk wani irin aiki na ta'addanci, kuma za ta tsaya tsayin daka kan goyon bayan kokarin da gwamnati da jama'ar Afghanistan suke yi na yaki da ta'addanci, da kiyaye zaman karkon kasar da tsaron jama'a. (Bilkisu)