A cikin sanarwar kwamitin ya jaddadda cewa, dole ne a hukunta wadanda suke bada taimakon kudi da goyon baya ga ayyukan ta'addanci da kuma wadanda suka aikata ayyukan, a sa'i guda ya kalubalanci dukkan kasashen duniya dasu hada kai tare da gwamnatin kasar Afghanistan da wasu bangarorin da abin ya shafa don sauke nauyin dake wuyansu, kamar yadda aka tanada cikin dokokin kasa da kasa da kudurorin kwamitin sulhun MDD.
Baya ga haka, kwamitin sulhun ya sake nanata cewa, duk wani irin ayyukan ta'addanci kalubale ne mafi tsanani dake kawo barazana ga zaman lafiya da tsaron kasa da kasa, tilas ne duk kasashen su yi iyakacin kokarin magance su. (Bilkisu)