A cikin sanarwar da ma'aikatar ta fitar, an ce mahara su 4 sanye da rigar dake makale da boma-bomai, sun kutsa cikin hotel din da karfe 9 na daren ranar 20 ga wata suka kuma bude wuta, nan take kuma aka fara bata kashi tsakanin su da sojojin tsaron kasar. A karshe dai sojojin tsaro sun ceto mazauna hotel din 160, ciki har da 'yan kasashen ketare 41.
A daren ranar 21 ga wata, ministan harkokin wajen kasar Ukraine Pavlo Klimkin ya tabbatar da cewa, jama'ar kasar sa 6 ne sun rasa rayukansu sakamakon farmakin da aka kai a hotel din na Intercontinental dake birnin Kabul. (Bilkisu)