in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD ta yi Allah wadai da harin otal a Kabul
2018-01-22 10:44:42 cri

Babban magatakardar MDD Antonio Guterres, da jagoran shirin majalissar dake tallafawa ayyukan jin kai a Afghanistan ko UNAMA a takaice Tadamichi Yamamoto, sun yi Allah wadai da harin da aka kaiwa otal din Intercontinental a birnin Kabul, fadar mulkin Afghan.

Cikin wata sanarwa da ya fitar a jiya Lahadi, Mr. Guterres ya gabatar da sakon ta'aziyya ga iyalan wadanda harin ya rutsa da su, tare da fatan samun sauki cikin sauri ga wadanda suka jikkata.

A kalla mutane 18 ne suka rasu, ciki hadda 'yan kasashen waje 14 a harin na birnin Kabul. An kuma ce dukkanin maharan 5 sun rasa rayukan su yayin musayar wuta da dakarun tsaron kasar. An dai shafe sa'o'i 12 ana dauki ba dadi kafin a kai ga kawo karshen mamayar maharan.

Tuni dai kungiyar Taliban ta dauki alhakin kaddamar da harin, tana mai cewa, maharan su 5 sun yiwa otal din tsinke, a wani mataki na kaddamar da hari kan jami'an gwamnati da baki 'yan kasashen waje dake cikin sa.

A wata sanarwar ta daban kuma, wakilin musamman na babban magatakardar MDD a Afghanistan Tadamichi Yamamoto, ya ce tsabar rashin tunani ne ya sanya mayakan Taliban kutsawa cikin otal din, kawai domin kaiwa fararen hula hari.(Saminu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China