Mutane 41 ne suka mutu, wasu 84 kuma suka jikkata bayan wasu jerin bama bamai sun fashe a cibiyar al'adu dake yammacin Kabul, babban birnin kasar Afghanistan.
Kakakin ma'aikatar lafiya ta kasar Wahid Majroh ya ce, daga cikin wadanda suka mutu sanadiyyar harin ta'addancin na jiya, akwai mata 4 da yara 2, sannan wasu mata 8 na daga cikin wadanda suka jikkata.
Harin ya auku ne da safe bayan 'yan ta'addan sun kai hari kan cibiyar al'adu ta Tebyan dake yankin Dasht-i-Barchi.
Kungiyar IS dai ta dauki alhakin kai harin. ( Fa'iza Mustapha)