in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Minista:Yunkurin juyin mulkin da aka murkushe a Equatorial Guinea wani lamarin ta'addanci ne daga ketare
2018-01-12 11:11:57 cri

Shafin Intanet na gwamnatin kasar Equatorial Guinea ya bayar da labari jiya Alhamis 11 ga wata, cewa ministan harkokin wajen kasar Agapito Mba Mkuy ya bayyana a Laraba cewa, ko shakka babu, yunkurin juyin mulkin da aka murkushe a kasar a karshen watan jiya, wani lamari ne na ta'addanci da aka kitsa daga ketare.

A cewarsa, ya zuwa yanzu dai gwamnatin kasar ta riga ta kama 'yan ta'adda 27, kuma kura ta riga ta lafa, sai dai kuma dumbin 'yan ta'addan suka tsere, yayin da wasun su ke samun mafaka a sassan gandun dajin da ke kan iyakar kasar ta Equatorial Guinea da kasashe makwabtan ta.(Kande Gao)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China